Gwamnatin Africa ta Kudu na lallashin jama'a da su daina kyamar baki
Gwamnatin kasar Africa ta kudu ta bukaci mutan kasar da su kwantar da hankula sakamakon kazamin boren kyamar baki da ake yi a wasu sassan kasar da ya kai ga kona shaguna da gidajen jama’a masu yawa.
Wallafawa ranar:
A dan tsakanin nan an sha samun rahotannin barnata kaddarorin baki sakamakon rashin ayyukan yi a fadin kasar.
A makon jiya sama da shaguna 20 aka barnata a yankin Atteridgeville a bayan garin Pretoria, yayin da gidajen baki 12 aka kaiwa hari a Rosettenville dake kudancin Johannesburg.
Ministan Harkokin cikin gida na kasar Africa ta Kudu Malusi Gigaba ya fadawa taron manema labarai cewa jama’a su dai kaiwa baki hare-hare.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu