Bakonmu a Yau
Dakta Kasimu Kurfi akan kudaden da aka kwato a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:00
A Yayin da hukumar EFCC a Najeriya ke ci gaba da kwato makudan kudaden da aka wawushe, wasu ‘yan kasar na korafi kan jan kafar gwamnati, wajen amfani da kudaden don ragewa al’umma radadin matsin da suke ciki. Sai dai kuma wasu masana tattalin arziki a kasar, sun ce abin ba haka yake ba, domin akwai matakai da dole sai an bi, kafin kudaden su zama mallakin gwamnati. Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dr Kasim Kurfi shugaban Kamfanin hada hadar hannayen jari na APT da ke Lagos.