Libya
An ceto bakin haure sama da 100 daga teku a Libya
Masu gadin gaban teku a kasar Libya sun yi nasarar ceto wasu bakin haure akalla 120 da kwale-kwaken su ya sami matsala a tsakiyar teku yau lahadi.
Wallafawa ranar:
Talla
Tun juma'a ne dai bain haure suka tashi daga garin Sabratha dake da nisan kilomita 70 daga birnin Tripoli, amma kuma suna cikin tafiya kwale-kwalen na su ya sami matsala.
Bayanai na nuna bakin hauren sun fito ne daga kasashe daban-daban daga nahiyar Africa.
Koda a jiya Asabar Hukumomin kasar Libya sun bayyana cewa sun kama bakin haure 400 dake neman tsallakawa turai ta teku.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu