Isa ga babban shafi
Nijar

An yi zanga-zangar adawa da gwamnati a Nijar

Dubban mutane ne suka fito zanga-zanga a Yamai babban birnin Jamhuriyyar domin adawa da tsadar rayuwa da kuma gwamnatin Mahamadou Issoufou. ‘Yan adawa da kungiyoyin fararen hula da malamai da daliban makaranta da ‘yan kasuwa ne suka shiga zanga-zangar ta lumana a Yamai.

'Yan adawa sun yi zanga-zangar tsadar rayuwa a Yamai
'Yan adawa sun yi zanga-zangar tsadar rayuwa a Yamai
Talla

Zanga-zangar kuma ta shafi yin adawa da girke dakarun kasashen Faransa da Amurka da Jamus wadanda suka kafa sansanoni a Nijar domin yakar ‘yan ta’ada a Libya da kuma Mali.

Zanga-zagar dai ta yi karo da wadda aka gudanar a watan Janairu domin nuna goyon baya ga gwamnatin Mahamadou Issoufou.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.