Isa ga babban shafi
Gambia

E. Guinea ta tabbatar da bai wa Jammeh Mafaka

Kasar Equatorial Guinea ta sanar da cewar ta bai wa tsohon shugaban kasar Gambia, Yahya Jammeh masauki bayan ficewar sa daga Banjul.

Tsohon shugaba Yahya Jammeh a lokacin ficewar sa daga Gambia
Tsohon shugaba Yahya Jammeh a lokacin ficewar sa daga Gambia ©Thierry Gouegnon/REUTERS
Talla

Ministan yada labaran kasar Eugenio Nse Obiang ya shaidawa manema labarai cewar Jammeh na kasar ba tare da cikkaken bayani kan halin da yake ciki ba.

Jammeh ya bar Gambia ne a karshen mako sakamakon matsin lamba daga kungiyar kasashen Afirka ta Yamma wadda ta tura dakarun ta Senegal dan tabbatar da cewar tsohon shugaban ya sauka daga mulki bayan kayen da ya sha a zaben da aka gudanar.

Kuma wannan shi ne karon farko da Guinea ke amsa bai wa Jammeh Mafaka.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.