Isa ga babban shafi
Amurka-Libya

Amurka ta kashe mayakan IS 80 a Libya

Sama da mayakan ISIL 80 ne jirgin yakin Amurka ya hallaka a sansaninsu da ke Libya, cikinsu akwai wadanda suke da hannu a shirya hare-haren ta’addanci da aka kai a wasu sassan kasashen Turai kamar yadda fadar gwamnatin Amurka ta Pentagon ta sanar.

Dakarun da ke yakar ISIL a Sirte
Dakarun da ke yakar ISIL a Sirte REUTERS/Ismail Zitouny
Talla

Sakataren tsaron Amurka Ashton Carter ya ce tabbas wadannan mutane suna kan shirya kaddamar da harin ta’addanci a Turai, Carter ya sanar da hakan ne a yayin da ya rage ‘yan sa’o’i ya bar aiki karkashin gwamnatin shugaba Barack Obama.

Kafin jiragen yakin Amurka su kaddamar da harin a maboyar mayakan da ke kudancin birnin Sirte an hango Su dauke da makamai suna gudanar da atisaye a sansanin na su.

Kafin daren laraba a kai harin kan mayakan na ISIL da ke barazana ga zaman lafiya a kasar ta Libya da ma sauran kasashen da ke makwabtaka da ita, kakakin ma’aikatar tsaron Amurka Peter Cook ya ce an sami gagarumar nasara a harin da aka kai kan mayakan

Amurka dai ta kai harin ne bisa umarnin shugaba Barack Obama mai barin gado tare da hadin-gwiwar gwamnatin hadakar Libya

Ana ganin nasarar kashe mayakan har 80 zai karya lagonsu na kai sabbin hare-hare kan dakarun kasar da ma fararren hula da ke aiki ba dare ba rana a kokarin samar da zaman lafiya a birnin na Sirte.

Libya ta fada cikin tashin hankali bayan rikicin juyin juya hali da ya kawo karshen mulkin marigayi kanar Ghadafi a shekarar 2011, tun daga wannan lokacin mayakan ISIL suka mayar da kasar mabuyarsu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.