An yi zanga-zangar goyon bayan gwamnati a Nijar
A jamhuriyar Nijar dubban mutane ne suka gudanar zanga-zangar nuna goyon baya ga shugaban kasar Issoufou Mahamadou wanda a kwanakin da suka gabata wasu kungiyoyin fararen hula da kuma ‘yan adawa suka gudanar da irin wannan zanga-zanga domin nuna rashin amincewa da salon mulkinsa.
Wallafawa ranar:
Zanga-zangar ta jiya ta samu halartar dubban mutane kamar dai yadda jam’iyyun siyasa kusan 50 da ke marawa shugaban kasar suka bukaci a yi.
A zanga-zangar da suka gudanar a kwanakin baya, 'yan adawa da kuma kungiyoyin fararen hula sun zargin shugaban kasar Issoufou Mahamadou da gazawa a cikin mulkinsa, yayin da suka yi zargin gwamnatinsa da yada rashawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu