Isa ga babban shafi
Kamaru

CPJ ta gargadi Kamaru kan musguna wa 'yan jaridu

Kungiyar da ke sa ido kan ayyukan ‘yan jaridu a duniya ta gargadi kasar Kamaru kan yadda ta ke  hana ‘yan cin fadin albarkacin baki da kuma musgunawa ‘yan jaridu.

Wakilin sashen hausa na RFI, Ahmed Abba da ke ci gaba da tsare a hannun hukumomin Kamaru
Wakilin sashen hausa na RFI, Ahmed Abba da ke ci gaba da tsare a hannun hukumomin Kamaru RFI
Talla

Kungiyar ta CPJ ta ce, a kwanan nan hukumomin Kamaru sun cafke wani dan jarida da ke daukan rahoto kan wata zanga-zanga, yayin da kuma suka dakatar da kafafan yada labarai da suka hada da gidajen rediyo da talabijin, baya ga sanya takunkumi kan wasu ‘yan jaridun da dama.

Wakilin kungiyar a yammacin Afrika Peter Nkanga, ya bukaci hukumomin na kasar da su gaggauta sakin wakilin gidan rediyon Faransa, Ahmad Abba.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da hukumomin kasar ke shirin gurfanar da Abba a gaban kotun soji a ranar 4 ga watan Janairu mai zuwa kan zargin alaka da Boko Haram, amma har yanzu an kasa gabatar da sheda akan haka.

Tun a ranar 30 ga watan Julin shekarar 2015 ne, aka kama wakilin na sahen hausa na RFI.

A bangare guda, ‘yan jaridun Kamaru sun bayyana cewa, a farkon wannan watan ne, gwamnatin kasar ta kuma haramta wa kafafan yada labarai masu zaman kansu, watsa muhawarar siyasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.