Isa ga babban shafi
Uganda

An cafke Sarkin da ake zargi da tinzira ‘yan banga a rikicin Uganda

Yan Sanda a kasar Uganda sun kama Sarkin wata kabila da ake zargi da tinzira magoya bayan sa wajen haddasa rikicin da ya hallaka mutane 55.

Yan sandan kasar Uganda 14 sun mutu a arangama tsakaninsu da 'yan banga.
Yan sandan kasar Uganda 14 sun mutu a arangama tsakaninsu da 'yan banga. Isaac Kasamani / AFP
Talla

Mai Magana da yawun Yan Sandan Andrew Felix Kaweesi ya ce an samu barkewar fadan ne a garin Kasese lokacin da masu tsaron Sarkin mai suna Charles Wesley Mumbere na Masarautar Rwenzururu suka kai hari kan jami’an tsaron dake sintiri, inda suka kashe Yan Sanda 14, yayin da Yan Sandan suka kashe masu gadin Sarkin 41.

Kakakin Yan Sandan ya ce suna zargin Sarkin da jagorantar kungiyar ‘yan bangan da suka yi sanadiyar mutuwar yan sandan kuma za su gurfanar da shi a gaban kotu.

Shugaban kasar ta Uganda  Yoweri Museveni ya bukaci rusa kungiyar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.