Isa ga babban shafi
Somalia

Gungun 'yan fashi a Somalia sun saki matukan Jiragen ruwa 26

Rahotanni daga Somalia sun ce, gungun masu fashi a teku sun saki matukan jiragen ruwa 26 da suka kama tare da tsare su tun a shekara ta 2012 tsibirin Seychelles da ke dab da kasar Madaskascar. 

Dan fashin teku a gaban jirgin Su da suka kwace a shekara ta 2012
Dan fashin teku a gaban jirgin Su da suka kwace a shekara ta 2012
Talla

Matukan Jiragen ruwan duka 'yan nahiyar Asia ne, daga kasashen China, Philippines, Cambodia, Indonesia, Vietnam da kuma Taiwan.

Matukan da suka tsallake rijiya da baya sune mafi dadewa a jerin wadanda ‘yan fashin tekun suka tsare a Somalia.

Matsalar fashi a teku na daya daga cikin abinda ke ciwa Somalia tuwo a kwarya, fama fama da matsalar hare-haren kungiyar al Shabab mai rajin kafa gwamnatin Musulunci a kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.