Kungiyar Lauyoyi ta yi allawadai da farmakin da aka kai wa Alkalai
Kungiyar lauyoyi a Najeriya ta soki dirar mikiyar da hukumar ‘Yan sandan farin kaya ta yi wa gidajen manyan alkalai a sassan kasar.
Wallafawa ranar:
A lokacin da ya ke mayar da martani Shugaban kungiyar Abubakar Mahmud ya ce sun yi allawadai da farmakin da ‘Yan sandan na farin kaya suka kai wa alkalan na Najeriya.
Mista Mahmud ya ce a mulkin dimukuradiya ba za su amince da irin wannan yanayin ba inda ‘Yan sanda za su abkawa gidajen Alkalansu na kotun koli da na babbar kotu.
Hukumar ‘Yan sandan na farin kaya dai ta ce ta kwato miliyoyan daloli a gidajen alkalan wadanda ta ke zargi da laifin karbar cin hanci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu