Isa ga babban shafi
Ethiopia

Mutane 52 ne suka mutu a tarzomar kasar Habasha

Rahotanni daga kasar Habasha na cewa mutane da dama ne suka rasa rayyukansu, sakamakon turmutsitsin da ya faru, a lokacin da ‘yan sanda suka yi amfani da harsasan roba domin tarwatsa tarzoma da barke a gefen wasu bukukuwan gargajiya da ‘yan kabilar Oroma suka yi a kasar a wannan lahadi.

Zanga-zangar 'yan Oromo a dandalin Meskel da ke Addis Abeba
Zanga-zangar 'yan Oromo a dandalin Meskel da ke Addis Abeba REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

An dai gudanar da bukukuwan ne da ake kira Irrecha a wani gari mai suna Bishoftu kamar dai yadda aka saba domin murnar girbe amfanin gonar bana, kuma kamar yadda gwamnan lardin da lamarin ya faru ke cewa, mutane 52 ne suka rasa rayukansu.

To sai dai 'yan adawa sun ce wadanda suka mutu sun fi mutane dari daya.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.