Isa ga babban shafi
DRC

Congo ta zargi Amurka da haddasa mata rikici

Gwamnatin Jamhuriyar Demokiradiyar Congo ta zargi Amurka ta kitsa tashin hankali a cikin kasar, bayan ta sanya wa wasu manyan jami’an shugaba Joseph Kabila takunkumi.

Wasu daga cikin 'yan adawar jamhuriyar Demokradiyar Congo
Wasu daga cikin 'yan adawar jamhuriyar Demokradiyar Congo AFP/EDUARDO SOTERAS
Talla

Ministan yada labaran kasar Lambert Mende ya ce, matakin da Amurka ke dauka a kasar ya yi kama da wanda ta dauka wajen jefa kasashen Libya da Sudan cikin rikicin da ke neman hallaka al’ummar kasashen biyu.

Ita dai Amurka ta sanya wa kwamandan sojin kasar Janar Gabriel Amisi Kumba da shugaban 'yan sanda janar John Numbi takunkumi ne saboda yadda jami’an tsaro ke kashe 'yan adawar da ke neman ganin an gudanar da zabe a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.