Amurka na adawa da tazarcen Kabila
Kasar Amurka ta bayyana cewar ba shugaban kasar Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo Joseph Kabila wa’adi na uku zai yi wa kasar babbar illa. Jakadan ma’aikatar harkokin wajen kasar Thomas Perriello ya ce akasarin kasashen da shugabaninsu suka sauya kundin tsarin mulki don ci gaba da zama karagar mulki sun fada cikin tashin hankali.
Wallafawa ranar:
Jakadan Congo Balumuene ya ce shugaba Kabila na bukatar Karin lokaci don ci gaba da yaki da ‘Yan Tawayen Tutsi tare da sake gina tattalin arzikin kasar.
Kabila ya karbi ragamar shugabancin Congo bayan kisan mahaifinshi a 2001 kafin kuma aka sake zaben shi a 2006 da 2011.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu