Guinea Bissau
ECOWAS zata fice daga Guinea Bissau
Kungiyar ECOWAS tace sojojin ta da suka samar da tsaro a kasar Guinea Bissau mai fama da juyin mulki zasu fice daga kasar nan da shekara guda.
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban gudanarwar kungiyar Marcel Alain De Souza ya ce babu dalilin ci gaba da zaman dakarun ECOWAS a kasar.
Shekaru 4 kenan dakarun na zaune a Guinea Bissau don tabbatar da cewa an samu tabbataccen tsaro a kasar.
De Souza yace cikin watanni shida masu zuwa sojojin kungiyar zasu cigaba da horar da takwarorin su na Guniea Bissau dan inganta tsaro a cikin gida.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu