Isa ga babban shafi
Najeriya

Yara sun kamu da Cutar Polio a Najeriya

Hukumar Lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya tace a karon farko bayan shekaru biyu an samu yara biyu da suka kamu da cutar polio a Najeriya, matakin da ya kawo koma baya dangane da shirin wanke kasar daga cikin masu fama da cutar.

Cutar Polio na haddasa  nakasa ga yara kanana
Cutar Polio na haddasa nakasa ga yara kanana AFP PHOTO / GWENN DUBOURTHOUMIEU
Talla

Hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya tace yara biyun sun kamu da cutar Polio a Jihar Barno wanda hakan ya mayar da hannun agogo baya a kokarin da Najeriya keyi na wanke kanta daga kasashen dake fama da cutar.

Matshidiso Moeti, Daraktan hukumar dake kula da Afirka tace abin abin yi yanzu shine tabbatar da cewar an yiwa yaran dake Yankin rigakafi cikin gaggawa.

Doune Porter, jami’in sadarwa na hukumar UNICEF a Najeriya yace samun bullar cutar a Maiduguri ya biyo bayan wahalar da aka samu wajen yiwa yara rigakafin cutar a Jihar dake fama da tashin hankali.

Shugaban kasar Muhammadu Buhari ya sha alwashin hada kai da hukumomin duniya dan tabbatar da kawo karshen cutar a Najeriya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.