Najeriya
An sace Hakimin Tama a Bauchi
Rahotanni daga Jihar Bauchi a Najeriya na cewa wasu ‘Yan bindiga sun yi awon gaba da Hakimin Garin Tama da ke karamar hukumar Toro Alhaji Adamau Yakubu. Bayan sace Hakimin kuma, ‘yan bindigar har ila yau sun sace wasu yara guda biyu ‘yayan wani dan kasuwa da ke garin na Tama.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni kuma sun ce akan hanyarsu ta fita garin na sun harbe wani mutun har lahira tare da raunata wasu a garin Lau da ke makwabtaka da garin Tama a Jihar Bauchi.
Babu dai wani cikakken bayani akan ko su waye ‘Yan bindigar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu