Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Ranar 6 ga Yuli za a yanke wa Pistorius hukunci

A ranar 6 ga watan Yuli kotun Pretoria za ta zartar da hukunci akan dan tseren guragun Afrika ta kudu Oscar Pistorius, da ke fuskantar shari’a kan tuhumarsa da ake da kisan budurwar shi a ranar masoya.

Tsohon zakaran gudun nakasasu Oscar Pistorius, ya cire kafafuwan shi na karfe a cikin harabar Kotun Pretoria
Tsohon zakaran gudun nakasasu Oscar Pistorius, ya cire kafafuwan shi na karfe a cikin harabar Kotun Pretoria REUTERS/Siphiwe Sibeko
Talla

Kotun ta tsayar da ranar yanke hukuncin ne bayan kawo karshen sauraren karar na kwanaki uku a jiya Laraba

Tsohon zakaran gudun nakasasu Oscar Pistorius, ya cire kafafuwan shi na karfe a cikin harabar Kotu a jiya Laraba, domin nunawa kotun bukatar sallama a maimakon ci gaba da tsare shi.

A jiya dai mahaifin Reeva Steenkamp wadda Pistorius ya kashe, ya bukaci a yanke hukunci mai tsanani saboda aikata kisan budurwar shi.

Lauyan Pitorius ya yi bahasi a kotun domin nuna nasakar dan tseren guragun a yanayin da zai iya kashe budurwar shi

A 2013 ne ranar masoya ta Valentine Pistorius ya bindige Reeva a gidan shi a tsakiyar dare amma ya yi ikirarin bude wuta tunanin wani ne ya yi kokarin kutsowa cikin gidan a cikin dare.

Mai shigar da kara ya bukaci a yanke wa Pistorius hukuncin dauri na akalla shekaru 15 a gidan yari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.