Isa ga babban shafi
Faransa-Najeriya-boko haram-Birtaniya

Kasashen duniya zasu taimakawa Najeriya wajen yakar Boko Haram

Da kamala taron kasa da kasa a Abuja,Shugabanin kasashen dake makwabtaka da Najeriya kama daga Nijar,Kamaru,Chadi,Benin sun sanar da hada karfi domin kawo karshen kungiyar Boko Haram.Yayinda Kasashen Duniya suka sanar da kawo nasu taimako a kai.

Francois Hollande Shugaban kasar Faransa da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Francois Hollande Shugaban kasar Faransa da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Francois Hollande wanda yake halartan taro na kasa- da-kasa gameda annobar Boko Haram, na magana da manema labarai bayan ya gana da Shugaban Najeria Muhammadu Buhari a birnin Abuja.

Faransa zata bada taimakon da ya dace wajen yakar kungiyar Boko Haram,hakka zalika Birtaniya da Amurka sun sanar da kawo nasu kokarin a kai.

Shugaba Hollande ya ce shakka babu anyi nasarar gaske wajen murkushe ‘yan kungiyar Boko Haram ya zuwa wannan lokaci.

Taron da ake yi a Abuja na samun halarcin shugabannin kasashen Benin, Kamaru, Chadi, da Niger wadanda dakarunsu ke cikin dakarun hadin guiwa 8,500 da za’a girke su a Chadi don share guggubin ‘yan Boko Haram da suka rage.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.