Rwanda
Zabtarewar kasa ta kashe mutane a Rwanda
Akalla mutane 20 akasarin su kananan yara zabtarewar kasa ta kashe a kasar Rwanda bayan a tafka ruwan sama kamar da bakin kwarya.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin ma’aikatar kula da agajin gaggawa ta kasar Frederic Ntawukuriryayo ya ce, zabtarewar kasar ta binne gidaje da dama a yankin Gakenke.
Kasar Rwanda mai dauke da tsaunuka na yawan samun ambaliya da zabtarewar kasar.
A cikin wannan shekarar kawai mutane 67 suka mutu, yayin da gidaje sama da dubu 1 500 suka rushe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu