Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Demokradiyar Congo

An sace ma'aikatan Red Cross 3 a Congo

Wasu mutane dauke da makamai sun sace ma’aikatan kungiyar agaji ta Red Cross guda 3 a Jamhuriyar Dimokraddiyar Congo, mai Magana da yawun kungiyar Elisabeth Cloutier tace an sace ma’aikatan ne a Rutshuru dake kudancin kasar inda suka je gudanar da aikin su.  

Ma'aikaciyar kungiyar likitoci ta MSF na kulawa da wani wanda ya sami rauni a Bangui
Ma'aikaciyar kungiyar likitoci ta MSF na kulawa da wani wanda ya sami rauni a Bangui REUTERS/Andreea Campeanu
Talla

Kakakin sojin kasar Capt Guillame Ndjike yace sun gargadi kungiyar da ta daina tura ma’aikata kauyuka ba tare da samun rakiyar jami’an tsaro ba.

Wannan dai bashi bane karon farko da ake sace ma'aikatan kungiyar  dake aikin agaji a kasashen Afrika, alkaluman kungiyar na cewa ma'aikatan kungiyar  60 ne suka rasa rayukansu a sassan Afrika a shekara guda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.