Najeriya
Sojin Najeriya sun kama wanda ya kashe Janar Shuwa
Rundunar Sojin Najeriya ta kame mutumin da ake zargi ya kashe Janar Mamman Shuwa daya daga cikin gwarzayen Sojin kasar da suka yi yakin basasa. Daraktan yada labaran rundunar Sojin Kanal Usman Kukasheka ya shaidawa RFI Hausa cewa za a gabatar da mutumin a gaban manema labarai a bataliya da uku a birnin Kano.
Wallafawa ranar:
Talla
A watan Nuwamban 2012 wasu ‘Yan bindiga da ake zargin ‘Yan boko Haram ne suka abka gidan Janar Mamman Shuwa a Maiduguri suka bude ma shi wuta dab da lokacin da ya ke shirin zuwa Sallar juma’a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu