Isa ga babban shafi
Chadi

Chadi ta tsawaita dokar ta-baci don fada da Boko Haram

Gwamnatibn Chadi ta tsawaita dokar ta-baci na tsawon watanni shida  domin dakile hare haren kungiyar Boko haram musamman a yankin tabkin Chadi. A jiya Talata ne Majalisar kasar ta amince da gagarumin rinjaye da matakin tsawaita dokar da aka kafa tun a 9 ga watan Nuwamba.

Shugaban Chadi Idriss Deby
Shugaban Chadi Idriss Deby REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

Ministan tsaro Ahmat Mahamat Bachir ya ce dokar za ta taimaka ga murkushe ayyukan Boko Haram a yankin Chadi.

Sannan Ministan ya ce za su inganta tsaro a ciki da wajen kasar zuwa sassan yankin tabkin Chadi.

‘Yan Boko Haram dai sun addabi Kauyukan da suka kewaye tabkin Chadi da hare hare. Sannan suna ratsowa cikin kauyukan domin shiga cikin kasar.

Rundunar hadin guiwa ta kasashen tabkin Chadi da aka kafa da ta kunshi dakaru daga Najeriya da Nijar da Chadi da Kamaru ta taimaka wajen murkushe‘Yan Boko Haram.

Sai dai har yanzu Boko Haram na ci gaba da zama barazana ga tsaron kasashen.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.