Isa ga babban shafi
Najeriya

Ba fada mu ke ba, Jayayya muke da Buhari- Ndume

Sanata Mohammed Ali Ndume shugaban masu rinjaye a majalisar dattijan Najeriya ya ce ba fada suke da shugaba Buhari  ba illa jayayya ga wasu fannonin da suke da sabani tsakanin bangaren Majalisa da zartarwa.

Sanata Mohammed Ali Ndume
Sanata Mohammed Ali Ndume thisdaylive
Talla

Wannan na zuwa ne bayan kungiyoyin fararen hula sun kaddamar da zanga-zanga domin adawa da ‘Yan majalisun Najeriya da suke zargin suna zagon kasa ga samun nasarar aiwatar da kasafin kudin bana a Najeriya.

Ndume wanda ke wakiltar Borno ta Kudu yace ba za su iya fada da shugabansu ba amma suna iya jayayya da shi kan bukatun da suke ganin ya dace a gyara.

A jiya Talata Masu zanga-zangar sun toshe hanyar zuwa Majalisa a Abuja tare yin kira ga shugaban Majalisar Dattijai Dr Bukola Saraki ya yi murabus.

Ndume yace babu wata girman zanga-zanga da za ta sa wani Dan Majalisa ya yi murabus. A cewar shi Zanga-zangar ta sabawa tsarin mulki domin akwai tsarin kiranye da ake yi akan duk wani Dan Majalisa.

Masu zanga-zangar dai sun bukaci ‘Yan majalisar su gaggauta kammala aikin da ya rataya akansu a kasafin kudin kasar, domin ba gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari damar aiwatar da ayyukan ci gaban raya kasa da ta yi alkawali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.