An kafa Majalisar Ministoci a Jamhuriyar Nijar
An kafa sabuwar majalisar ministoci mai mambobi 38 a jamhuriayr Nijar, kwanaki 10 bayan rantsar da Issoufou Mahamadou akan wa’adin mulkin kasar karo biyu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sabuwar majalisar ministocin wadda aka sanar da kafawa a cikin daren jiya, ta kumshi tsoffi da kuma sabbin fuskoki a cikinta, domin 15 daga cikin tsoffin ministoci da suka taba yi aiki da gwmanatin da ta gabata sun dawo a cikin gwamnatin.
Dukkan jam’iyyun da ke da wakilci a majalisar dokokin kasar sun samu mukamai a wannan sabuwar gwamnati, yayin da aka damka sauran mukaman a hannun wadanda suka dafawa Shugaba Issoufou domin samun nasara a zaben shugabancin kasar zagaye na biyu.
Tsohon ministan harkokin wajen kasar Bazoum Mohamed ne aka nada a matsayin ministan cikin gida, yayin da aka mika ragamar ma’aikatar tsaron kasar a hannun Hassoumi Massaoudou wanda shi ne ministan cikin gida a gwamnatin da ta gabata.
Tsohon mataimakin daraktan mulki a fadar shugaban kasar, wanda kuma ya tsaya takarar a zaben shugabancin kasar Ibrahim Yacouba ne aka bai wa mukamin ministan harkokin waje.
Wasu daga cikin sabbin fuskoki a gwamnatin sun hada da Kassoum Moctar tsohon magajin garin Maradi da aka bai wa ma’aikatar gidaje, sai Lawan Magaji a matsayin ministan ayyukan jinkai, yayin da ministan albarkatun mai Foumakoye Gado da takwaransa na ma’aikatar kudi Seidou Sidibe suka ci gaba da rike mukamansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu