Isa ga babban shafi
Djibouti

Shugaba Ismail Omar Guelle na Djibouti ya Sake Lashe Zaben Kasar

Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh , wanda yake shugabancin kasar tun shekara ta 1999 ya sake lashe zaben kasar da aka gudanar Juma’a, karo na hudu a jere.

Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh
Shugaban kasar Djibouti Ismail Omar Guelleh AFP PHOTO/Carl de Souza
Talla

Hukumomin kasar sun bayyana cewa Shugaban kasar ya sami yawan kuriu kashi 86.68% na yawan kuriu da aka jefa.

A jawabin sa Shugaban kasar mai shekaru 68 ya godewa al'ummar kasar saboda sake zaben sa da akayi.

A shekara ta 2011 Fira Ministan kasar  ya sanar da nasarar shugaban kasar ta su a zaben kasar  tun kafin a kammala tattara kuri'u, amma kuma tunda akace shugaban kasar mai shekaru  ya sami yawan kuri'u fiye da kashi 50% sai aka sanar da cewa ya lashe.

Mutane dubu 187 ne suka chanchanci jefa kuria a zaben daya gabata a fadin kasar.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.