An rantsar da Issoufou na Nijar
A yau Asabar aka rantsar da shugaban Nijar Mahamadou Issoufou a wa’adin shugabanci na biyu bayan ya lashe zaben kasar zagaye na biyu da aka gudanar a ranar 20 ga watan Maris mai cike da kalubale.
Wallafawa ranar:
An gudanar da bikin rantsar da shugaban ne dai a birnin Yamai fadar gwamnatin Nijar a gaban shugabannin kasashen Afrika kimanin 9 da suka halarci bikin.
Issoufou ya rantse da al Qaur’ani mai tsarki bayan ya samu nasara da kashi 92.51 na kuri’a a zaben da ‘yan adawa suka kaurace.
A cikin jawabin shugaban bayan rantsar da shi ya jaddadda cewa zai mayar da hankali wajen yaki da ta’addanci tare da kokarin magance wasu matsalolin ‘yan Nijar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu