Ebola-Saliyo
Ebola-An killace sama da mutane 100 a Saliyo
Gwamnatin Kasar Saliyo ta bukaci al’ummar kasar su kwantar da hankalin su bayan ta sanar da killace mutane sama da 100 saboda mu’amala da wata mata mai shekaru 22 da ta mutu sakamakon cutar Ebola.
Wallafawa ranar:
Talla
Hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce matar ta mutu ne a garin Magburaka dake kusa da iyakar kasar Guinea, inda 'yan uwanta suka mata jana’iza ba tare da sanar da hukumomin lafiya ba.
Ishmael Tarawally, jami’in gwamnatin kasar ya ce har yanzu akwai wasu mutane 3 da ake nema ruwa a jallo.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu