Isa ga babban shafi
Najeriya

Shekaru 50 da kisan su Sardauna da Tafawa Balewa

Yau juma’a 15 ga watan Junairu, shekaru hamsin kenan da akayi juyin mulki na farko a Najeriya, inda sojoji suka kashe Firaministan kasar Sir Abubakar Tafawa Balewa da Firamiyan jihar Arewa sir Ahamadu Bello Sardaunan Sokoto.

Sir Ahmadu Bello
Sir Ahmadu Bello
Talla

Tun daga wannan lokaci har zuwa yanzu,yankin  arewa da al'ummominta ba su farfado daga kidimewar da ta same su ba sakamakon wancan mummunan al'amari.

Da dama daga cikin yan kasar na ci gaba da alfahari da nasarorin da Gwamnatin lokacin ta samu tareda dora yankin arewa a kan tafarkin ci gaba da zaman lafiya.

An dai haifi Sa Ahmadu Bello a ranar 12 ga watan Yuni na shekarar 1910 a wani gari da ake kira Rabba a cikin jihar Sakkwato dake arewacin  Najeriya.

Tarihi ya nuna cewa kakan sa shi ne Sarkin musulmi Malam Bello,wanda  ya kasance daya daga cikin mutanen da sukka kafa daular Musulunci ta Sakkwato a wancan karnin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.