Isa ga babban shafi
Gabon

Jean Ping na AU zai shiga takara a zaben Gabon

Tsohon Shugaban kungiyar kasashen Afirka ta AU, Jean Ping ya bayyana aniyarsa ta shiga takarar shugabancin kasar Gabon domin kawo karshen mulkin shugaba Ali Bongo.

Tsohon Shugaban hukumar Tarayyar Afrika Jean Ping
Tsohon Shugaban hukumar Tarayyar Afrika Jean Ping REUTERS/Noor Khamis
Talla

Ping ya ce bukatarsa ita ce kawo sauyi da yadda ake gudanar da shugabancin kasar don tabbatar da gaskiya da sanya wa’adin shugabancin da kuma zuba jari a bangaren kiwon lafiya da ilimi da kayan more rayuwa.

Ping dai na kokarin kawo karshen shekaru 50 da Jam’iyya mai mulki ta shafe tana shugabanci a Gabon.

A zaben 2009 ne Ali Bongo ya gaji Mahaifinsa Omar Bongo da ya rasu.

A watan Agusta mai zuwa ne za a gudanar da zaben kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.