Wasu ‘Yan bindiga sun karbe makamai daga hannu Dakarun AU
Wasu ‘Yan bindiga da ba a tantance ba sun kai wa dakarun wanzar da zaman lafiya na Afrika harin kwantar bauna a yankin Darfur na Sudan inda suka karbe makamai da bindigogi daga hannunsu.
Wallafawa ranar:
Lamarin da ya faru a ranar Alhamis a jihar Arewacin Darfur yammacin Sudan, inda dakarun Afrika da na Majalisar Dimkin Duniya ke aikin wanzar da zaman lafiya.
Rundunar Afrika tace akwai sojanta guda da ya samu rauni, amma ba tare da bayar da cikkaken bayani ba.
Kasashen Afrika dake ruwa da tsaki a batun kasar Sudan sun dai tir da allah wadai tareda yi kira bangarori daban daban na gani sun dawo kan teburin tattaunawa.
Yan gudun hijira da dama yanzu hakka ke cikin mauyacin hali,karancin cimaka da sauren su a yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu