Isa ga babban shafi
Afrika ta Kudu

Afrika ta kudu za ta shigar da tan miliyan 5 na masara

Rahotanni daga kasar Afirka ta kudu sun ce kasar za ta shigar da tan miliyan 5 na masara domin cike gibin karancin abincin da ake fama da shi a kasar sakamakon matsalar farin da aka samu a kakar bana.

Fari ya janyo wa Afrika ta Kudu asarar tan miliyan 10 na masara
Fari ya janyo wa Afrika ta Kudu asarar tan miliyan 10 na masara Reuters
Talla

Jannie de Villiers, shugaban hukumar samar da abinci a kasar ya danganta matsalar farin da aka samu da sauyin yanayi wanda ya sa aka yi asarar kusan ton miliyan 10 na masara da ake nomawa a kasar.

Jami’in ya ce kasar na cikin mawuyacin hali a yanzu haka.

Ko a watan jiya sai da hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da matsalar abinci a daukacin kasashen da ke kudancin Afirka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.