Isa ga babban shafi
Najeriya

An yi yunkurin halaka Burutai a Zaria

Sojojin Najeriya da kungiyar musulmi mabiya akidar Shi’a na zargin juna da haifar da rikicin da ya kai ga rasa rayukan mutane da dama a garin Zaria cikin Jihar Kaduna a jiya Asabar.

Babban Hafsan Sojin Najeriya Janar Tukur Burutai
Babban Hafsan Sojin Najeriya Janar Tukur Burutai army via twitter
Talla

Rundunar sojin Najeriya na zargin mabiya shi’a da yunkurin halaka babban hafsan sojin Kasar Janar Tukur Burutai a lokacin da ayarinsa ke kan hanyar zuwa fadar Sarkin Zazzau.

A yayin da kuma bangaren kungiyar Shi’a a Zaria ta musanta zargin tare da zargin sojin kasar da kashe mabiyanta ba wani dalili.

A cikin wata sanarwa, kakakin rundunar Sojin Najeriya Kanal Usman Kukasheka yace ‘Yan shi’ar sun toshe hanyar da babban hafsan Sojin zai wuce zuwa fadar Zazzau inda suka kona tayu dauke da adduna da duwatsu.

Kukasheka yace Sojoji sun kare kansu bayan mabiyan sun abkawa tagawar babban Hafsan sojin ta Najeriya Turkur Burutai.

Mutane da dama ne dai aka ruwaito sun mutu a arangamar da aka yi tsakanin Sojoji da mabiyan na Shi’a a garin Zaria.

Rundunar Sojin Najeriya tace an 'Yan Shi'a sun nemi halaka Janar Burutai a Zaria

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.