Isa ga babban shafi
Kamaru

Mata sun kai harin kunar bakin wake a Kamaru

Akalla mutane 7 suka mutu a wasu hare haren kunar bakin wake da mata biyu suka kai a garin Dabanga cikin Arewacin Kamaru a jiya Assabar. Daga cikin wadanda suka mutu har da matan biyu ‘yan kunar bakin wake.

Wannan ne karon farko da aka kai harin kunar bakin wake a Dabanga cikin arewacin Kamaru
Wannan ne karon farko da aka kai harin kunar bakin wake a Dabanga cikin arewacin Kamaru
Talla

Gwamnan yankin arewa mai nisa Midjiyawa Bakary, ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa akwai sojojin Kamaru biyu da suka samu rauni.

Wannan ne dai karon farko da aka kai hare haren kunar bakin wake a Dabanga da ke kusa da Kousseri kan iyaka da Najeriya.

Arewacin Kamaru dai na cikin yankin da mayakan Boko Haram na Najeirya suka addaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.