Isa ga babban shafi
Mali

An kashe Sojojin MDD 3 a Mali

Kungiyar Mayakan Ansar Dine masu da’awar Jihadi a Mali ta yi ikirarin daukar alhakin harin roka da aka kai a sansanin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya.

Sansanin Sojin Majalisar Dinkin Duniya a Kidal arewacin Mali
Sansanin Sojin Majalisar Dinkin Duniya a Kidal arewacin Mali REUTERS/Adama Diarra
Talla

Mutane uku suka mutu a harin da suka kunshi Jami’an wanzar da zaman lafiya guda biyu da wani farar hula guda, sannan kimanin 20 suka jikkata a harin na Kidal.

Harin na zuwa ne duka mako guda da aka kai wani mummunan hari a wata Otel a Bamako babban birnin kasar Mali.

Majalisar Dinkin Duniya ta la’anci harin, yayin da kwamitin tsaro ya danganta harin a matsayin laifukan yaki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.