Isa ga babban shafi
Najeriya

Matsayin INEC kan makomar APC a zaben Kogi

Hukumar zaben Najeriya INEC ta ce tana jiran Jam’iyyar APC ta sanar da ita a hukumance game da rasuwar dan takararta na gwamna a zaben Jihar Kogi Prince Abubakar Audu wanda ya rasu kafin a kammala zaben.

Dan takarar Gwamnan Jihar Kogi a Jam'iyyar APC Prince Abubakar Audu wanda ya rasu a ranar Lahadi bayan kammala zaben gwamnan Kogi a ranar Assabar
Dan takarar Gwamnan Jihar Kogi a Jam'iyyar APC Prince Abubakar Audu wanda ya rasu a ranar Lahadi bayan kammala zaben gwamnan Kogi a ranar Assabar naijanewsmag
Talla

A hirarsa da RFI Hausa, Kakakin Hukumar Nick Dazang ya ce har yanzu suna sauraren APC akan rasuwar Prince Audu.

Mista Dazang ya ce sai idan APC ta sanar da su sannan za su diba dokokin zabe da tanadin da kundin tsarin mulki suka tanadar kan idan haka ta faru.

01:42

Kakakin Hukumar INEC Nick Dazang

Bashir Ibrahim Idris

“ Za mu yi amfani da kundin tsarin mulki da dokokin zabe domin tabbatar da adalci”, a cewar Nick Dazang.

Dan takarar gwamnan na APC Prince Abubakar Audu ya rasu ne bayan hukumar zabe tace ba a kammala zaben Jihar Kogi ba da aka gudanar a ranar Assabar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.