Isa ga babban shafi
Najeriya

Ana zaben gwamnan jihar Kogi a wannan asabar

Rundubnar ‘yan sandan tarayyar Najeriya ta sanar da takaita zirga-zirga a duk fadin jihar Kogi da ke tsakiyar kasar, domin tabbatar da cewa an gudanar da zaben gwmana da ake gudanarwa a wannan asabar.

'Yan takarar zaben gwamnan jihar Kogi a Najeriya
'Yan takarar zaben gwamnan jihar Kogi a Najeriya
Talla

Babban sufeton ‘yan sandan kasar Solmon Arase ya bayyana a wata sanarwa cewa an hana zirga-zirgar ababan hawa daga karfe 6 na safe zuwa 6 na marecen yau asabar hatta ga masu ratsa jihar zuwa wasu yankuna na Najeriya.

An dai tsaurara matakan tsaro a wannan zabe da ake karawa tsakanin gwamnan jihar mai-ci Idris Wada na jam’iyyar PDP da kuma Abubakar Audu na jam’iyyar APC.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.