Isa ga babban shafi
Nijar

PNDS ta tsayar da Issoufou a zaben Nijar

Jam’iyyar PNDS Tarayya mai mulki a Jamhuriyar Nijar ta bayyana shugaba Mahamadou Issoufou a matsayin dan takararta a zaben shugaban kasa da za a gudanar a badi.

Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou
Shugaban Nijar Mahamadou Issoufou AFP Photo/Brendan Smilalowski
Talla

Shugaban Jam’iyyar PNDS Bazoum Mohamed yace sun yaba da jagorancin Issofou kuma sun  amince ya ci gaba da jagorantar kasar domin ya samu damar idar da ayyukan da ya dauko don ci gaban ‘Yan Nijar.

Yanzu shugaba Issoufou shi ne na uku daga cikin ‘Yan takarar da suka bayyana kudirin tsayawa takara a zaben shugaban kasa da za a gudanar a watan Fabrairun 2016. Daga cikin ‘Yan takrarar kawai Hama Amadou babban mai adawa da Shugaba Issoufou da kuma tsohon Minista Amadou Boubacar Cisse, wadanda dukkaninsu suka marawa Issoufou baya a zaben 2011 zagaye na biyu.

01:48

Lydia Ado ta aiko da rahoto game da taron PNDS

Lydia Ado

Amma ana ganin zaben Nijar na badi zai kasance mafi inda Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira a gudanar da karbabben zabe cikin kwanciyar hankali, musamman yanzu da kasar ke fama da barazanar Boko Haram.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.