Isa ga babban shafi
Cote D'ivoire

ICC ta dage shari'ar Laurent Gbagbo

Kotun hukunta manyan laifufuka ta duniya ICC, ta dage shari’ar da ake yi wa tsohon shugaban kasar Cote d’Ivoire Laurent Gbagbo zuwa ranar 28 ga watan Janairu na shekara mai zuwa.

Tsohon shugaban Cote d'Ivoir Laurent Gbagbo
Tsohon shugaban Cote d'Ivoir Laurent Gbagbo AFP PHOTO/ POOL/ MICHAEL KOOREN
Talla

Kotun ta ce ta dage sauraron karar zuwa shekara mai zuwa ne domin bai wa alkalan kotun nazari kan bayanan lafiyar tsohon shugaban.

Matsayin kotun na zuwa ne ranar da hukumar zaben Coted’Ivoire ta bayyana Alassane Ouattar a matsayin wanda ya lashe zaben kasar.

Ana tuhumar Gbagbo mai shekaru 70  bisa aikata lainfin cin zarafin al-umma bayan ya haifar da rikicin siyasa lokacin da ya ki amince wa da shan kayi a takarar da ya yi da Ouattara a shekara ta 2010.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.