Nijar
Boko Haram ta kashe Sojojin Nijar biyu a Diffa
Sojojin Nijar biyu aka kashe a harin kunar bakin wake da mayakan Boko Haram suka kai a wani kauye da ke cikin yankin Jihar Diffa a kudu masu gabashin kasar a yau Laraba.
Wallafawa ranar:
Talla
Maharan sun kai harin ne a kauyen Blangouri da ke kusa da garin Diffa a cikin dare.
Ministan tsaron Nijar Mahamadou Karidjo ya ce jami’an tsaron kasar sun yi nasarar kashe ‘Yan ta’addan tare da tarwatsa makamansu. Amma a cewarsa Sojojin Nijar biyu suka mutu kuma wasu sun samu rauni.
Boko Haram dai ta jima tana kai hare hare a yankin Diffa da ke cikin dokar ta-baci.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu