Isa ga babban shafi
Chadi-Najeriya-Nijar

Chadi ta tabbatar da mutuwar mutanen 41 a harin Baga Sola

Gwamantin Kasar Chadi ta sanar da cewar mutane 41 ne suka mutu sakamakon hare- haren da kungiyar Boko Haram ta kai kasuwar Baga Sola da ke kusa da iyakar Najeriya, yayin da wasu 48 suka samu raunuka.

Dakarun kasar Chadi dake fada da kungiyar Boko Haram a kan iyaka da Kamaru
Dakarun kasar Chadi dake fada da kungiyar Boko Haram a kan iyaka da Kamaru AFP PHOTO / STEPHANE YAS
Talla

Rahotanni sun ce an kai harin ne a kasuwa da kuma sansanin 'yan gudun hijira da suka tserewa garuruwan su saboda hare-haren kungiyar.

Yanzu haka hukumomin lafiya na ci gaba da kula da wadanda suka samu raunuka a harin.

Kungiyar Boko Haram sun sake kai wasu jerin hare-hare a garin Kangaleri da ke da nisan kilometa 30 da garin Mora a kasar Kamaru a jiya lahadi.

Gwamnatin Kamaru ta bayana alhini ta, a cewar kakakin Gwamnatin kasar Issa Tchiroma wanda ya ce kungiyoyin fararen hula su bayar da hadin kai ga hukuma domin kawo karshen ta'adanci a kasashen Tafkin Chadi                                                                                                                                                                                     

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.