Isa ga babban shafi
Liberia-Ebola

Liberia ta sake kubuta daga cutar Ebola

Hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta sake bayyana cewa Kasar Liberia ta kubuta daga cutar Ebola.

Jami'an dake yaki da cutar Ebola a Liberia
Jami'an dake yaki da cutar Ebola a Liberia REUTERS/Daniel Berehulak/The New York Times/
Talla

Hukumar ta sanar da haka ne a yau Al-hamis bayan kwanaki 42 da aka gudanar da bincike kan mutum na karshe da ake zaton na fama da cutar.

A watan Mayun daya gabata ne Hukumar lafiyar ta ce Liberia ta kubuta daga cutar yayin da ta sake bullowa bayan makwanni 6 da sanarwar.

Hukumar dai ta yaba da kokarin da Liberia ta yi na daukan matakan gaggauwa domin yakar cutar bayan mutane 6 su kamu da ita tare da kashe mutane 2 dabam.

Kasar Liberia dai na cikin jerin kasashen yammancin Afrika da cutar ta fi yiwa illa tun loacin da ta yadu sosai a shekarar 2013 , inda ta kama mutane dubu 28 tare da kisan sama da mutane dubu 11 a kasashen Guinea da Saliyo harma da Liberia.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.