A yau daya ga watan Satumba ne aka rantsar da Dr Akinwumi Adesina a matsayin sabon shugaban Bankin Raya Kasashen Afirka, a wani gagarumin biki da aka gudanar a birnin Abidjan na kasar Cote D’Ivoire.
Akinwumi Adesina wanda tsohon ministan aikin gona na tarayyar Najeriya, ya karbi ragamar tafiyar da bankin ne daga hannun Donald Kaberuka, wanda ake yabawa jagorancin sa na shekaru 10.
Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Farfesa Kabiru Isa Dandago, masani tsarin tattalin arziki, kuma kwamishinan kudi na jihar Kano a tarayyar Najeriya, domin jin irin kalubalen da ya kamata sabon shugaban bankin na ADB ya tunkara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu