Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari ya damu kan rikicin mulkin Kasar Guinea Bissau

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana damuwar sa kan rikicin mulkin da ake fuskanta a kasar Guinea Bissau inda ya bukaci al’ummar kasar su mutunta kundin tsarin mulki.

Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari
Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari AFP PHOTO / STRINGER
Talla

Mai baiwa shugaban kasar shawara kan harkokin yada labarai Femi Adeshina yace shugaba Buhari ya tura tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo zuwa kasar dan sasanta shugaba Jose Mario Vaz da Firaminsita Domingos Pereira.

Akan hanyar sa ta zuwa kasar, Obasanjo ya gana da shugaban kasar Senegal Macky Sall dake shugabancin kungiyar kasashen Afirka ta Yamma, dan yi masa bayani.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.