Najeriya
Wata ta kai harin kunar bakin wake a Maiduguri
Wata ‘Yar kunar bakin wake ta tayar da bom a kasuwar Gamburo kwastam a garin Maiduguri cikin keke Napep da safiyar yau Juma’a. Wakilin RFI Hausa Bilyaminu Yusuf wanda ya tabbatar da harin yace an samu hasarar rayuka.
Wallafawa ranar:
Talla
Bilyaminu ya ce kimanin mutane biyar suka mutu tare da jikkata wasu da dama, kuma adadin wadanda suka mutu na iya karuwa.
‘Yar Kunar bakin waken ta kai harin ne sanye da hijabi cikin karamar mota mai kafa uku da ake kira Keke napep.
Zuwa yanzu Jami’an tsaro sun killace inda aka kai harin a garin Maiduguri.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu