Isa ga babban shafi
Masar

Za a daure masu bayar da bayanan da ke saba wa na gwmanati

Gwmanatin Masar na shirin kafa sabuwar doka da ke bayar da damar daure duk wani dan jarida da ya wallafa alkalumman ‘’karya’’ game da dakarun kasar da suka mutu sakamakon harin ta’addanci.

Abdel Fattah Al-Sissi, shugaban Masar.
Abdel Fattah Al-Sissi, shugaban Masar. REUTERS/The Egyptian Presidency/Handout
Talla

Wannan dai na kunshe ne a cikin wani sabon daftarin doka da gwamnatin kasar ke shirin kafawa domin kawo karshen yadda ake samun bambancin alkalumma tsakanin na hukumomi da kuma wadanda ‘yan jarida ke bayarwa a duk lokacin aka kai wa jami’an tsaron kasar hari.

Yanzu haka dai gwamnatin Abdel Fatah Al-sisi ya kuduri aniyar murkushe duk wadanda ke neman yi wa gwmnatinsa hawan kawara, da suka hada da ‘yan adawa da kuma ‘yan jaridu.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.