Dan kunar bakin wake ya kashe mutane 6 a cocin Potiskum
A Najeriya wani dan kunar bakin wake ya kai hari tare da kashe mutane akalla 6 a wata mujami’a da ke wajen birnin Potiskum na jihar Yobe a daidai lokacin da masu ibada ke gudanar da addu’o’i a yau lahadi.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce maharin ya shiga cocin ne da ke unguwar Jigawa a garin na Potiskum, inda nan take ya fasa bam din da yake dauke da shi, kuma daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da daya daga cikin fastocin da ke jagorantar addu’o’in.
Shaidu sun ce ko baya ga wadanda suka rayukansu akwai wasu mutane da dama da suka sami raunuka a cikin wannan coci da ake kan ginawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu