Maroko
Bakin haure sun nemi mafaka cikin mujami'a da ke Tanger a Maroko
Daruruwan baki ‘yan ci rani da ke kokarin shiga Turai ne suka nemi mafala a wata mujami’a da ke yankin Tanger na kasar Maroko, domin kauce wa jami’an tsaro da ke kokarin kama su.
Wallafawa ranar:
Talla
Tun a farkon makon da ya gabata ne jami’an tsaron suka kaddamar da samame domin kama dimbin baki da ke kokarin tsallakawa zuwa Turai daga kasar, yayin da sauran suka ruga zuwa cikin wannan coci da ke garin na Tanger.
Mafin yawansu dai matasa ne mata da maza da suka fito daga kasashen Afirka na yankin kudu da Sahara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu