Isa ga babban shafi
Guinea-Conakry

Bensouda na binciken kisan fararen hula a birnin Conakry

Yau asabar babbar mai shigar da kara ta kotun duniya Fatou Bensouda za ta kammala ziyarar da take gudanarwa a birnin Conakry na kasar Guinee, inda kotun ke gudanar da bincike a game da kisan da sojojin kasar suka yi wa fararen hula 157 a ranar 28 ga watan satumbar shekara ta 2009.

Fatou Bensouda, mai shigar da kara ta kotun duniya da ministan shari'ar Guinea Cheik Sako a birnin Conakry, ranar 3 ga watan yulin 2015
Fatou Bensouda, mai shigar da kara ta kotun duniya da ministan shari'ar Guinea Cheik Sako a birnin Conakry, ranar 3 ga watan yulin 2015 AFP PHOTO / CELLOU BINANI
Talla

A watan okotobar bara ne ya kamata Bensouda da kuma sauran masu bincike daga kotun su kasance a birnin Conakry, to sai dai sakamakon bullar cutar Ebola a kasar sai a dage wannan ziyara.

Binciken ya zo ne a daidai lokacin da tsohon shugaban gwamnatin mulkin sojan kasar wanda a lokacin mulkinsa ne aka aikata wannan kisa Keftin Moussa Dadis Camara ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara a zaben shugabancin kasar da za a gudanar a watan oktoban bana.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.