Isa ga babban shafi
Burundi

Mutane 6 sun mutu a rikicin Burundi

Akalla mutane shida aka kashe cikin su har da Dan Sanda guda a ci gaba da tashin hankalin da ake samu a kasar Burundi inda al’ummar ke dakon sakamakon zaben ‘Yan Majalisun da aka gudanar a kasar.

Zanga-zangar adawa da matakin shugaba Nkurunziza na neman wa'adin shugabanci na uku
Zanga-zangar adawa da matakin shugaba Nkurunziza na neman wa'adin shugabanci na uku Reuters
Talla

Rahotanni sun ce fada ya barke ne a unguwar Cibitoke da ke birnin Bujumbura, wanda ya ke sansanin ‘Yan adawa ne ma su adawa da takarar shugaban kasa Pierre Mkurunziza.

Amma ‘Yan Sanda sun ce rikicin ya barke ne tsakanin kungiyoyin ‘yan bindiga.

Mutane sama da 70 suka rasa rayukansu a rikicin siyasar kasar da aka kwashe watanni biyu ana yi, yayin da kuma kusan mutane 150,000 suka tsallaka zuwa makwabtan kasashe saboda fargabar barkewar yakin basasa.

Rikicin siyasa dai ya barke ne a Burundi bayan da shugaban kasar Pierre Nkurunziza ya bayyana aniyarsa ta neman wa’adin shugabanci na uku.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.